BABBAN LABARIN
HOLLYWOOD
 
STEPHANIE OKEREKE
 

KOTU TA BIYA MATA BUKATA

AUREN JARUMA STEPHANIE OKERERE YA RUGUJE. TA FAD'A WA MUJALLAR FIM CEWA TA KOYI BABBAN DARASI DAGA RIKICIN AUREN TA

Daga SANI MAIKATANGA da IBRAHIM MUSA GIGINYU

A DUK lokacin da aka furta irin badak'alar da ta shafi aurataiya na ’yan fim a wannan k'asar, wala’Allah finafinan Hausa ne ko na Turanci (wato Kannywood ko Nollywood) sai ka ji ana cewa, “Da ma haka su ke”. Wannan shaidar ta cewa maza da mata ma’abota wannan sana’ar ba su d'auki aure a bakin komai ba, shaida ce mai matuk'ar illa ga su

’yan fim d'in. Hasali ma wasu na ganin cewa yadda mazan su ka d'auki aure kamar sa hula ne -- ka sa dara yau, gobe ka sa zanna. Ga matan kuma abin kamar yin kitso ne, yau ki yi d'aure-d'aure gobe kuma a yi zane.

Masu karatu sun sha karantawa a shafukan wannan mujallar yadda auratayya da mutuwar auratayyar 'yan fim ke kasancewa. Idan ba ku manta ba a watannin baya mun kawo maku wani labari game da jarumar nan fitacciya ta Nollywood, wato Stephanie Okereke, har ta shaida mana cewa a kasuwa ta ke. Wata majiya mai k'arfi ta shaida mana cewa a wannan lokacin jarumar su na kotu ne da mijin ta. Domin ita jarumar ta rubuta takardar neman kotun da ta raba auren nata da mijin ta, wani tsohon d'an wasan k'wallon k'afa na Super Eagles wai shi Chikelue Illonyosi.

Jarumar, wadda ta tab'a shiga cikin jerin sunayen wad'anda su ka sami nasarar shiga cikin gasar jarumar jarumai mata a gasar AMAA, ta shaida wa majiyar mu cewa cin amana da yaudara na daga cikin dalilan da take son kotu ta duba wajen raba wannan auren. Ita dai wannan jarumar sun yi auren su ne a ciki Agusta 2004 a Legas. An d'aura auren cikin rashin sanin cewar mijin nata na da wata matar mai suna Ijeoma Mba a can Amerika. Kai, har ma da wasu ’yan matan da ya ke nema barkatai. Ta k'ara da cewar a lokacin da ta tuntub'i mijin nata kan wannan batun, bai mata musun hakan ba. Sai dai wannan maganar ba ta yi masa dad'i ba domin maganar sai da ta jawo ita jarumar ta sha na jaki a gun mijin.

A lokacin da Illonyosi ya ke maida martani kan zargin da Okereke ke yi masa kan cewa ya yi mata sama da fad'i da wasu kayayyakin ta, ya ce jarumar ta yo hayar wasu zauna gari banza wad'anda su ka far wa gidan nasu su ka kuma yi awon gaba da kayayyakin sa. Ya shaida wa kotu cewa zargin da jarumar ke yi masa na wai ta na bin sa kayayyaki na miliyoyin naira da kuma batun ita ke kula da gida da kuma d'aukar d'awainiyar gidan, duk zuk'i ta malle ce kawai.

Cikin k'orafin da ta mik'a wa kotu, Okereke ta buk'aci da kotu ta umarci mijin da ya biya ta zunzurutun kud'i har naira miliyan 100 a matsayin diyyar wahalar da ta sha a sakamakon wannan watsi da kuma yaudara da ya yi mata. Haka zalika ta buk'aci kotu da ta umarce shi da ya dawo mata da wasu kayayyaki na mak'udan kud'i. Sun had'a da mota Marsandi k'irar CLR 500 wadda aka k'iyasta za ta kai naira miliyan uku da rabi, da kuma wata motar Baswaja Passat 2.0 mai lamba DP 182 GGE wadda ita ma aka k'iyasta za ta kai naira miliyan uku da rabi. Akwai kuma komfuta laptop wadda za ta kai N150,000. Sauran kayayyakin su had'a da firji, gas kuka, tukwane da wasu kayan, wad'anda aka k'iyasta su kan N600,000. Cikin sauran kayayyakin da jaruma ke son kotu ta karb'a mata akwai wasu karnuka gudu uku.

To amma duk da wannan badak'alar, Illonyosi ba ya son wannan rabuwar. Amma kasancewar shari’a sab'anin hankali, daga k'arshe dai kotu ta raba wannan auren. Stephanie Okereke dai an zama bazawara.
Da mujallar Fim ta tuntub'e ta ta waya a daidai lokacin da mu ke daf da had'a wannan labarin a kan wannan al’amarin, sai jarumar ta ce, “Gaskiya ban ji dad'i ba a ce aure na ya mutu cikin k'ank'anin lokaci haka, to amma na koyi darasi. Ina kuma farin ciki da wannan darasi da na koya. Ka ga nan gaba sai in yi taka-tsatsan wajen zab'ar miji.”

RAYUWAR IYALI
BABBAN LABARIN
 
 

WASIKU
Ku daina wulakanci
Ai ga irin ta nan!
Mu taya sani addu’a
Abin a yaba ne
Allah ya gafarta ma ta
Allah ya jikan jamila
Allah ya jikan binta
Sakon ta’aziyya da jaje
Ta’aziyya ga sheme
Ki canza rayuwar ki
Allah ya gafarta ma ta
Sako ga shehu kano
Mu ma mun sara mata
’Yan fim ga shawara
Dubi dai jamila haruna
jaje da ta’aziyya
Allah jikan rai
Aikin ku ya yi kyau
Matashiya ga ummancy
‘bolanle’ shirme ne
Ku hada ni da ali nuhu
Rashin ya shafi kowa
Allah ya ba sani lafiya
Sakon ta’aziyya
Fati nijar ta birge ni
Gaisuwa ga ma’aurata
Ku daina la’antar su
Ki na fa da aure!
Rabo mayaudari ne
Allah jikan su
Tahir da binta ina murna
A gaida nakwango
Fantimoti ga gyara
Na ga alfanun fim

LABARAI
An yi taron addu’a ga mamatan marubuta a Kano
’Yan fim na Katsina sun kai wa Rabo caffa
Kotu ta haramta wak'ok'in industiri guda 11
Jami’an Rabo sun fara farautar mawak'a
An Kama Ali Jita Saboda Wak'ar Biki
Mahaifiyar Safiya Musa Ta Kwanta Dama
Ummi Zee-Zee ta zama mawak'iyar Turanci
Zainab da Rabi’u Dalle sun samu Umar
K'ungiyar dillalai na so a raba ta da zalunci
An bugi ’yan fim an hana su kuka
 
   
 
An fara buga mujallar Fim (ISSN 1595-7780) a cikin Maris 1999. Ta na fitowa a kowane wata daga kamfanin INFORMART PUBLISHERS LTD., No. AK 6, Yoruba Road, Kaduna, Nijeriya. Ofishin mu a Kano: Ofishin mujallar Concern, 2nd Floor, Hadiza House, daura da Masallacin Umar Ibn Khattab, Zaria Road, Kano.
A aiko da dukkan wasiku ta adireshin mu na I-mel: mujallarfim@yahoo.com