LABARAI
An yi taron
addu’a ga mamatan marubuta a Kano

RAN Lahadi, 7 ga Yuni 2009, ’ya’yan K'ungiyar Marubuta
ta K'asa (ANA), reshen Jihar Kano, su ka yi taron tunawa da kuma
addu’a da karatu na musamman ga ’yan’uwan su marubuta
da su ka rasu. An shirya taron ne a d'akin taro na Murtala Muhammed
da ke Kano. Da misalin k'arfe 10:00 na safe aka bud'e taro da addu’a,
wanda Malam Sadi Mandawari ya yi.
Jawabin farko ya fito ne daga
bakin shugaban rik'o na k'ungiyar ta ANA, wato Dr. Yusuf Adamu,
inda ya yi godiya da ’ya’yan k'ungiyar suka samu damar
halartar taron. Bayan nan, sai shugaban taron, Farfesa Saleh Abdu,
ya yi jawabi dangane da mamatan.
An gabatar da addu’o’i na musamman, wanda Malam Lawan
Adamu Giginyu ya jagoranta, wato mawallafin mujallar ‘Zamani’.
Har ila yau, samari sun gabatar da k'asidu da gajerun wak'ok'i ga
wasu daga cikin ’ya’yan wannan k'ungiya su ka rubuta,
kuma su ka karanta, wad'anda su ka shafi gudunmuwar su a fannin
adabi.
An dai tashi daga taron lafiya da misalin k'arfe uku na yamma.
Mamatan da aka yi wa wannan taro na musamman su ne Malama Binta
S. Mohammed (wato maid'akin Ibrahim Sheme), da Abdullahi Muktar
Yaron Malam, Abubakar Ishaq, Bashir Farouk Roukbah, da A’isha
Usman Bugaje.
Wasu daga cikin wad'anda su ka halarci taron sun had'a da Bala
Anas Babinlata, Badamasi S. Burji, Dr. Tanko, Dr. Hafizu Miko Yakasai,
da dai sauran su. Malama Maryam Ali Ali ita ce wakiliyar shugaban
ANA na k'asa a wurin.
’Yan
fim na Katsina sun kai wa Rabo caffa
Daga SANI MAIKATANGA
RANAR Laraba, 10 ga Yuni 2009, ne shugabannin ’yan fim na
Jihar Katsina su ka kai wa Darakta Janar na Hukumar Tace Finafinai
ta Jihar Kano, Malam Abubakar Rabo, ziyara a ofishin sa da ke Kano.
Tawagar ta iso Kano da misalin k'arfe 2:00 na rana, a k'ark'ashin
jagorancin babban sakataren k'ungiyar MOPPAN, reshen Jihar Katsina,
Malam Abubakar Suleiman Saiwan. ’Yan tawagar sun had'a da
mataimakin sakataren k'ungiyar, Malam Hamisu Lawal, sai Nana Garba,
Abubakar Ayuba, da Isma’il Abba Masanawa, sai kuma shugaban
k'ungiyar furodusoshi ta Jihar Katsina, Malam Rabi’u M. Yaro,
da shugaban k'ungiyar daraktoci ta jihar, Mustapha B. Mohammed,
Lawal Sa’idu, Hassan Isah, Kamal U.K. Soro, Jamilu S. Hameed,
Abubakar M. Sadiq, Lawal Usman, da kuma Abdul’aziz A. Alibaba.
Jagoran tafiyar, Malam Abubakar Sulaiman, ya shaida wa wakilin
mu cewa sun kawo ziyarar ne domin shimfid'a kyakkyawar dangataka
da kuma mik'a wuya ga hukumar game da irin jagorancin da ta ke yi
a k'ark'ashin jagorancin Malam Abubakar Rabo. Sai kuma neman alfarma
a kan wata matsala da ta shafi wata ’yar wasa da yawancin
furodusoshi su ka sa a finafinan su, amma aka nuna ba za a duba
finafinan ba saboda jarumar ba ta yi rajista ba. “Duk da dai
mun ji dai an ce ta yi, amma ba a kammala tantance ta ba. To a nan
mu na neman alfarma da a taimaka mana a duba finafinan ’ya’yan
mu. Kuma an yi hakan ne ba tare da sani ba. Amma nan gaba za mu
duba mu tabbatar da duk wanda za mu sa a finafinan mu, sai mun tabbatar
da ya na da shaidar kammala rajista da ita hukumar.
“Sannan mu na rok'on duk wani d'an mu ya zamanto ya nuna
takarda daga wurin mu kafin a duba finafinan sa, don gudun samun
matslala. Wanda yanzu haka mun taho da wad'annan takardun domin
nuna wa ita wannan hukumar irin su.”
Jim kad'an bayan tattaunawar, sai tawagar ta isa ofishin Rabo.
Bayan an bud'e taron da addu’a, sai aka ba su dama kowa ya
gabatar da kan sa. Sannan aka saurari jawabin abin da ke tafe da
su daga bakin Abubakar Suleiman. Bayan nan sai Malam Rabo ya gabatar
da nasa jawabin.
Ya fara da yi wa sababbin shugabannin fatan alheiri. Ya yi kira
da su sanya al’amurran da su ke yi a kan tsari na addini da
al'ada mai kyau a cikin finafinan su. Ya kuma yi alk'awarin ba su
goyon baya, da tabbatar da ci-gaba. Ya kuma sake shaida masu cewa,
domin tabbatar da ci gaba da tsari mai kyau da ba da goyon baya
ga masu shirya fim na Katsina.
Shugaban ya yi masu alk'awarin sa su a cikin tsari nataron k'ara
wa juna sani (workshop) da hukumar za ta yi wa ’yan fim na
Kano nan ba da dad'ewa ba. Ya buk'ace su da su ba da mutum biyu
daga jihar su don shiga tsarin, amma idan har sun tabbatar da cika
sharud'd'an da aka gindaya masu.
Kotu ta haramta
wak'ok'in industiri guda 11
KOTUN ’yan fim, wadda ke k'ark'ashin Hukumar Tace Finafinai
da D'ab’i ta Jihar Kano, ta haramta saurare ko yad'a wasu
wak'ok'i guda 10 da ’yan fim su ka k'irk'ira a fad'in Jihar
Kano.
Babban majistare Mukhtari Ahmed ne ya yanke wannan hukuncin a ranar
3 ga Yuni, 2009, tare da bayyana cewa haramcin ya fara aiki ba tare
da b'ata lokaci ba.
Wak'ok'in da aka haramta d'in dai su ne:
1. “Hasbunallahu” ta su Aminu Ala
2. “Rabo-Rabo” ta Maryam A. Baba
3. “Sank'arau” ta Sa’id Ishaq Gobinda
4. “An Cuce Mu” ta Bello Billy
5. “Dawo-dawo” ta Nazifi Asnanic
6. “Jigida” ta Nazifi Asnanic
7. “Girgiza Kai” ta Naziru Hausawa
8. “Ibro Sauka a Mashin” ta ?
9. “Kukan Ibro” ta ?
10. “Kan Mai Uwa Da Wabi” ta Adam A. Zango
11. “Kowa Ya Ci Ubansa/Uwarsa” ta
A cewar alk'alin, wak'ok'in su na d'auke da batsa ne, da yak'ar
hukuma, sannan sun sab'a wa tarbiyya tagari. Ya ce kotun za ta hukunta
duk wanda aka samu ya na yad'a wak'ok'in, ko ya na sauraron su,
ko ya na kwafar su daga wata na’ura.
Ya ce ya yanke wannan hukunci ne bisa tanajin Sashe na 97 na dokar
da ta kafa Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano ta shekarar 2001
da kuma dokar gidajen kallo ta dai ita wannan shekarar.
Alk'ali Ahmad ya bayyana cewa kamar yadda dokar ta tanada, duk
wani mutum da aka kama ya na sayar da wani abin kallo ko na saurare
ko na karantawa wanda ya k'unshi sab'o, tsiraici ko batsa da zai
iya lalata tarbiyyar jama’a, to za a gurfanar da shi a gaban
kotun.
Ban da haramta wak'ok'in da aka yi, jami’an hukumar sun kai
samame a wasu kamfanonin buga wak'ok'i, amma ba su ci nasarar kama
kowa ba.
Wani darakta da bai so a ambaci sunan sa ya yi kokwanton manufar
hukumar kan haramcin sauraren wad'annan wak'ok'in. Ya ce, “Su
hangen su hakan ne zai gyara tarbiyyar Musulmin Jihar Kano. Sai
dai ga duk ma’abocin hankali, abin kamar an yi baya ba zani
ne, domin daga cikin wak'ok'in da aka haramta d'in babu wak'ar Barmani
Coge, babu ta Ali Makaho, babu ta Sani D'an Indo, Babu ta Mai Asharalle,
Babu ta Makosa, babu ta Kerewa, babu ta Micheal Jackson ko Bob Marley.
“A b'angaren yayin rufe kamfanonin buga wak'ok'i da shagunan
sayar da finafinai ma haka al’amarin yake. Domin duk rufe-rufen
da ake yi har yau ba a rufe gidan sinima ko d'aya ba. Har yau su
na nan su na gyaran tarbiyya da finafinan Turawa, Indiya, Canis
da kuma na kudancin Nijeriya. Ga DSTV a kowane otal ko babban gida.
Bahaushe ya ce da ma wargi wuri gare shi. Ana tsoron inna inji ’ya’yan
mayya! Ashe dai ko Baba da Baban sa.”
Jami’an Rabo
sun fara farautar mawak'a
AN ce idan lalacewa ta taso wa kare, sai ya daina cizo ya koma
tunkuyi. Da alama Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano ta fara fuskantar
k'arancin aikin yi dangane da kakkab'ar ’ya’yan kad'anyar
da ta ke yi wa ’yan fim. A bayyane yake cewa duk wanda ya
amsa sunan sa a cikin harkar fim a Kano, hukumar ta karya shi da
k'arfin iko. ’Yan fim dai tun su na d'an iya tagazawa, har
sun hak'ura, kowa ya kama gaban sa. Tun ana samun na kamawa har
ta kai ga ba a ma ganin su ballantana maganar kamu ta taso. To kun
san masu iya magana sun ce da zaman banza, gara aikin banza.
Tunda yake ana k'amfar ’yan fim, yanzu hukumar ta karkata
akalar ta zuwa ga mawak'a. Sai dai wasu mawak'an sawun b'arawo su
ka taka. A ranar Alhamis, 4 ga Yuni, 2009, kotun hukunta ’yan
fim ta Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano ta yi wa mawak'a shiri
na musamman, inda ta kai farmaki wuraren da ake buga wak'ok'i, har
ta samu nasarar cafke wasu mawak'an, ta yi awon gaba da su. A ranar
ne aka kulle kamfanin buga wak'ok'i na Hikima Multimedia da ke kan
Zoo Road a nan Kano.
Bayanai a kan dalilin rufe kamfanin sun kasu gida biyu. Na farko
dai an ce ma’aikatan su na zargin cewa a wurin ne aka buga
wak'ar da ta fi kowace wak'a tayar masu da hankali, wato ‘Hasbunallahu’,
wadda su Aminu Ala su ka yi. Kuma ta na d'aya daga cikin wak'ok'in
da a yanzu haka aka haramta jin su a fad'in Jihar Kano. A wani b'angaren
kuma aka ce sun rufe wajen ne saboda laifin rashin sabunta rajistar
kamfanin.
Sai dai kamar yadda wata majiya mai tushe ta shaida mana, duk abin
an yi shi ne saboda zargin a wurin ne aka buga ‘Hasbunallahu.’
A ranar Lahadi, 6 ga Yuni 2009, jami’an hukumar sun yi wa
Hikima dirar mikiya tun da sanyin safiya. An ce sun je da k'wararrun
masana komfuta, wad'anda aka yi amfani da su wajen binciken komfutocin
da ke wajen, ana neman gano idan a wajen ne aka yi wak'ar. Amma
haka su ka gama binciken su su ka bar wurin hannu rabbana. Sannan
tun farkon zuwan jami’an, babu wanda su ka fara nema sai Aminu
Ala, wanda kusan shi ne jagoran rukunin mawak'an na ‘Hasbunallahu’,
kuma manajan kamfanin. A lokacin Ala ba ya nan. Don haka sai su
ka nemi ganin Sani Salisu Yakasai, wanda ke rik'e da muk'amin manajan
darakta na wurin, shi ma ba a same shi ba.
Ban da wannan, sai kuma masoya da abokan arzik'i su ka yi ta buga
wa mawak'an waya su na gargad'in su da cewa kar su bari su yi tozali
da jami’an Hukumar Tace Finafinan, domin kama su ake nema
a yi. Wannan ya sa ganin mawak'an ya yi wa wakilan mu wuya don jin
ta bakin su. Sai dai wakilin mu ya samu tattaunawa da su ta wayar
GSM. Mutum na farko da ya fara samu, Bashir D'and'ago, ya ce lallai
ya na da masaniya kan wannan dambarwar. “K'warai, ina sane.
Mutane da dama sun kira ni ta waya su na gaya min an rufe Hikima
saboda wak'ar Hasbunallahu.”
Kan zancen ’yar b'oyo da mawak'an su ka fara yi don gudun
kamu, sai ya ce, “Ni ba wani b'oyo da na ke yi. Ina nan ina
yawo a gari. Kuma duk mai nema na ya san inda zai gan ni, don ni
ba b'oyayye ba ne a cikin garin Kano. Kuma yau duk wanda ya saurari
rediyon Kano ya ji murya ta, mu na wani shiri har na tsawon awa
d'aya.”
To amma me ya sa tun da can ba a kulle Hikima ba sai bayan wata
wak'a da mawak'a fiye da 50 daga Kano su ka je Kaduna su ka yi,
su na rok'on Darakta Janar na Hukumar Alhazai ta jihar, Alhaji Sani
Lawan K'ofar Mata, ya tsaya masu takarar kujerar gwamna a zab'en
2011? Anya siyasa ba ta shiga cikin al’amarin nan ba kuwa?
Adamu Kirfi, wanda ya na d'aya daga cikin mawak'an na ‘Hasbunallahu’,
ya amsa wannan tambayar da cewa, “Kai ma ka san akwai siyasa
a ciki, musamman ganin irin rungumar da mu mawak'a mu ka yi masa.
Kuma ba ma mu ba, duk wanda ya san Sani Lawan a Kano zai yi masa
abin da mu ka yi masa in ya na da hali. Domin Sani Lawan mutum ne
mai tausayi da son taimakon jama’a. Don haka ni a fahimta
ta, ana so ne a tab'o Sani Lawan, aka kuma lab'e da wak'ar ‘Hasbunallahu’.”
Yanzu menene abin yi?
“Ba mu da wani abin yi illa mu bi yadda dokar k'asa ta tsara
na neman hak'k'i idan aka tauye wa mutum,” cewar Kirfi.
Shi kuwa uban tafiyar, wato Aminu Ala, mun tambaye shi, shin da
ma ya na da masaniyar zuwan ma’aikatan ne, shi ya sa ya k'i
zuwa ofis a ranar? Ya ce, “Ni da ma a lokacin ina kan hanya
ta ta zuwa Katsina. Na bar wurin kenan aka ce sun zo. Waya aka yi
min ana shaida min ga abubuwan da ke faruwa. Bayan na dawo kuma
sai masoya su ka rik'a bugo min su na shaida min cewa in aka gan
mu kama mu za a yi.”
Hikima dai kamfanin Alhaji Sani Lawan K'ofar Mata ne. Shi me ya
ce dangane da al’amarin? Sai Ala ya ce, Wallahi tun da na
shigo Kano na ke neman layin shi amma har yanzu ban same shi ba.”
Sai dai bincike ya nuna duk ruwan su na k'ok'arin k'arewa ne a
kan Ala. Domin su kan su jami’an na Hukumar Tace Finafinan
shi su ke son yin tozali da shi, ko me ya sa? “To, ni ma abin
ya na d'aure min kai. An ce an dakatar da wak'ok'i har guda goma.
Amma me ya sa ba a neman wad'anda su ka rera sauran wak'ok'in sai
dai Aminu Ala kawai? Ka ga wannan abin tambaya ne,” cewar
Ala. To ko dai akwai siyasa a cikin al’amarin? Mawak'in sai
ya kada baki ya amsa da cewa, “Ba abin mamaki ba ne, musammana
yadda su ka ga irin d'aukakar da Allah Ya yi wa shi Alhaji Sani
Lawan d'in. Don haka in ma an ce akwai siyasa a ciki ni ba zan musa
ba.”
Ko akwai matakin da mawak'an ke shirin d'auka game da wannan badak'ala?
Misbahu M. Ahmad ya amsa tambayar da cewa, “Ai mu ba mu da
wani mataki da za mu d'auka da ya wuce mu bar komai ga Allah. Idan
mutum ya na jin giyar mulki ta na d'ibar sa ya na wulak'anta jama’a,
wata rana ya na ji ya na gani sai dai ya ga ana yi. Mu mun dogara
ga Allah, kuma za mu ci gaba da gaya wa Allah,
shi zai ba mu mafita.”
Wakilin mu ya yi iyakar k'ok'arin tattaunawa da Sani Salisu Yakasai,
wato babban manajan Hikima Multimedia, don jin ta bakin sa, amma
ya ce shi ba zai iya cewa komai ba. Abin da kawai ya sani shi ne
an kulle
Hikima an kuma bud'e.
Wannan al’amari dai yanzu haka ya sanya mafi yawancin mawak'an
barin mahaifar su zuwa gudun hijira a wasu garuruwan; wasu na Kaduna,
wasu Jos, wasu Abuja. Kai, akwai ma wanda ya na tashi daga Kano
ba inda ya zame sai Lokoja, inda ba ya da dangin uwa balle na uba.
Ya naji ya na gani mahaifar sa ta gagare shi zama.
Wani abu da ya d'aure wa ’yan fim kai shi ne mafi yawancin
mutanen da hukumar ke farauta su na daga cikin wad'anda su ka yi
rajista da hukumar. Masu lura da al'amurran yau da kullum a fagen
shirin fim sun sha hasashen cewa yin rajistar ba zai yi wani alfanu
ba. In ba ku manta ba, a Fim ta watan Nuwamba 2008, mu ka bugo jerin
sunayen ’yan fim da ake sa ran da d'ai d'ai da d'ai d'ai za
a kama su. Har a wancan lokacin Ali Nuhu ya yi azarb'ab'in k'aryata
mu a jaridar Sunday Trust ta ranar Lahadi, 16 ga Nuwamba 2008.
Sunayen da mu ka buga a wancan lokacin cewa wata k'wak'k'warar
majiya ta shaida mana cewa Rabo na so ya kama su ne:
1. Ibrahim Mandawari
2. Sani Mu’azu
3. Ahmad Alkanawy
4. Ado Gidan Dabino
5. Saratu Gid'ad'o
6. Ali Nuhu
7. Sani Masu Danja
8. Falalu D'orayi
9. Naziru Hausawa
10. Aminu Ala
11. Dakta Ahmad Sarari
12. Rabi’u Ibrahim (Daushe)
13. Rabi’u Ibrahim (HRB)
14. Jamila Haruna Yakasai
15. Adam A. Zango
16. Kabiru Arayu
17. Maryam Sangandale
18. Balaraba Ramat Yakubu
19. Mamman Mutu-ka-raba
20. Abdulhadi Awilo
21. Isma’il I.U.I.
22. Maryam Fantimoti
23. Aminu Maidawayya
24. Aminu Bala (Mugu)
25. Bala Anas Babinlata
26. Aminu Ahmed (Saira)
27. Sadi Sidi Sharifai
28. Fati Nijar
29. Murja Baba
30. Rasheeda Adam
31. Ashiru Nagoma
32. Dakta Umar Faruk Jibril
A wancan lokacin, mun shaida maku cewa ba su kenan ba.
AN KAMA ALI JITA SABODA
WAK'AR BIKI
Daga ALIYU A. GORA II
IN ta bi daga-daga, na k'urya ka sha kashi! Masu hankali da yawa
daga cikin ’yan fim tuni su ka fahimci cewa kiran da ake yi
masu na cewa su je su yi rajista da Hukumar Tace Finafinai ta Jihar
Kano da ke k'ark'ashin jagorancin Abubakar Rabo duk yaudara ce.
Don haka yawanci su ka cika cika rigunan su da iska su ka canza
gari. Wasu kuwa, tuni su ka mik'a wuya su ka amsa kiran, saboda
sa ran za a iya d'aga masu k'afa su ci gaba da sana’ar su
tunda sun yi biyayya. Ashe abin ba haka ya ke ba. Hasali ma dai,
wasun su sun gane su kan su kiwon ragon layya ake yi masu, domin
yin rajistar bai yi masu maganin abin da su ke jin tsoron ba.
Ali Jita, d'aya daga cikin mawak'a masu tashe, ya yi rajista da
su Rabo, tare da amincewa da duk lokacin da ya yi sabuwar wak'a,
zai kai wa hukumar su duba don tantancewa kafin ya sake ta, kamar
yadda ita hukumar ta umurci mawak'an da su rik'a yi. To amma duk
biyayyar da Ali ya yi ba ta taimake shi ba, domin a ranar Alhamis,
4 ga Yuni, 2009, kotun hukunta ’yan fim ta Hukumar Tace Finafinai
ta Jihar Kano ta kama mawak'in a kan wata wak'a da ya yi ta biki,
ba ma ta fim ba. “Sun kama ni ne a kan wata wak'a ta biki
da na yi. Kuma wak'ar ma ina da satifiket d'in da su su ka ba ni
kafin in sake ta. Kuma na nuna masu satifiket d'in. To ka san su
in su ka kama ka, ko ka na da gaskiya sai ka je can ka yi masu bayani,”
inji Ali Jita a lokacin da ya ke tattaunawa da wakilin mu bayan
an sako shi.
Da yawa ana ganin cewa jami’an Rabo sun yi wa Ali Jita kamun
wulak'anci ne. Domin kamar yadda ya ce, “Sun kira ni ta waya
ne, a lokacin ina tare da mata ta, mun fito daga unguwa zan kai
ta gida. Da su ka kira ni, sai su ka ce su na situdiyo na, su na
so in zo zan nuna masu wata takarda. Ina zuwa na tarar da ’yan
sanda da bindigogi sun zagaye wajen. Su ka kama ni, su ka tafi da
ni. Tun wajen k'arfe 3 (na yamma) har dare ina hannun su, kuma duk
mata ta ta na tare da ni. To da zan kwana ma, sai alk'alin ya taimake
ni ya zo cikin dare, k'arfe 9:00 na dare aka yi shari’ar.
Ya yanke min hukuncin wata biyu a gidan yari ko in biya tarar N15,000.
Sai na da biya su ka sake ni.” Ali ci gaba da bayyana cewa
ya na ganin maganin wannan wulak'acin kawai shi ne ’yan fim
su tattara su bar garin Kano in su na son su tsira da mutucin su.
Ya ce shi ma ya na ganin zai gangara zuwa Kaduna ya samu wuri ya
ci gaba da sana’ar sa tunda su na da gwamna mai son jama’a
da adalci. A wani labarin kuma, duk da a ranar, wani fitaccen mawak'in,
wato Aminu Maidawayya, shi ma ya tsallake rijiya da baya. Domin
shi ma maridan Rabo sun kai masa hari, amma sai su ka yi rashin
sa’a ba su same shi ba. Duk da haka an ce sun kulle masa ofis.
Tun daga ranar wakilan mu su ke neman shi ta waya, amma har aka
tafi buga wannan mujallar babu wanda ya ji d'uriyar sa ballantana
a ji ta bakin sa.
Mahaifiyar Safiya
Musa Ta Kwanta Dama
INNA lillahi wa inna ilaihi raji’un! A ranar Litinin 1, ga
Yuni 2009, ita ce ranar da shahararriyar jaruma Safiya Musa za ta
iya kira bak'ar rana, domin a ranar ne ta yi rashin abin da ba za
ta iya samun madadin sa ba har abada. A ranar ne Allah Ya yi wa
mahaifiyar ta Malama Hadiza Musa Makka rasuwa a gidan su mai lamba
25, Badarawa Road, Unguwar Shanu, Kaduna, da misalin k'arfe 8:30
na dare.
Mama Hadiza ta rasu ne sanadiyyar ciwon tarin fuka (asthma) da
na zuciya. Kafin rasuwar ta, marigayiyar sai da ta yi jinya a wani
asibiti mai zaman kan sa mai suna Dana Clinic da ke tsohon filin
jirgin sama na Kaduna har na tsawon mako d'aya. Bayan ta samu sauk'i
an sallame ta da kwana shida sai kuma ciwon ya dawo mata. Aka sake
d'aukar ta zuwa asibitin sojoji na ‘44’ da ke unguwar
Badikko, kan hanyar zuwa Tudun Wada, Kaduna. A nan kuma kwanan ta
d'aya kacal ta samu sauk'i, aka sallame ta, ta koma gida. Bayan
kwana biyar da sallamar ta ne Allah Ya yi mata cikawa.
Amma duk bidirin da ake yi Safiya ba ta gari, sai dai aka kira
ta aka shaida mata rasuwar.
Mama Hadiza ta rasu ta bar mijin ta Alhaji Musa Makka da ’ya’ya
biyar -- namiji d'aya, sauran kuma duk mata. Daga cikin ’ya’yan,
Safiya ce ta hud'u. Marigayiyar ta bar jikoki bakwai - maza uku
mata hud'u.
Da yake cikin daren Litinin d'in ne ta rasu, ba a yi jana’izar
ta ba sai da safiyar Talala, 2 ga Yuni. Da yake labarin bai shiga
industiri da sauri ba, babu wani d'an fim da ya samu jana’izar.
Sai dai daga baya ’yan fim sun yi ta yin jerin gwano zuwa
yi wa Safiya da ’yan’uwan ta gaisuwa. Sun had'a da Ummi
Nuhu, wadda ita ce ’yar fim da ta fara zuwa gidan, sai Ubale
Wanke-wanke, wanda ya wakilci Sani Danja, da ya ke shi ma ya na
kwance ba lafiya; Yakubu Muhammad, Ibrahim Maishunku, Rasheeda Adam,
Yusuf Maina, A’isha Abubakar ZIAU, Jamilu Kocila, Abubakar
Yerima, Yakubu Lere, Nura Mado, Kawu Kamfa, Isma’il Na’abba
(Afakallahu), Abubakar Musa Anka, Nasiru Anchau, da Rabi’u
Ibrahim HRB.
Allah ya gafar wa Malama Hadiza Musa Makka, amin summa amin.
Ummi Zee-Zee ta
zama mawak'iyar Turanci
D'AYA daga cikin al’amuran da takurawar da Hukumar Tace
Finafinain ta Jihar Kano ta yi wa industiri ya haifar shi ne rikid'ar
’yan fim da dama. Da yawan su, musamman mawak'a, sun fito
fili su na yin fayafaye (wato albums) su na sayarwa. Haka kuma wasu
’yan wasa sun zama mawak'a duk da yake ba a tab'a zaton za
su zama mawak'an ba.
Babu ma kamar Ummi Ibrahim (Zee-Zee), kyakkyawar jaruma wadda ta
jima ba a ji d'uriyar ta ba, tun daga dai labarin bikin kewayowar
ranar haihuwar ta wanda mu ka ba ku a Fim ta Maris 2008. To, ana
zaton wuta a mak'era sai ta tashi a masak'a. Zee-Zee ta zama zabiya!
Wak'ar kuma ba ta Hausa ta koma yi ba, a’a irin wak'ok'in
nan ne na Turanci irin na ’yan kudancin Nijeriya. A yanzu
haka Zee-Zee ta nan ta na k'ok'arin fito da album d'in da ta yi
a k'ark'ashin wani kamfani mallakar wasu Inyamirai a Legas mai suna
Townsquare Music. An ce kamfanin mallakar fitaccen mawak'in nan
ne d'an k'abilar Ibo mai suna Timaya.
Kwanan baya Zee-Zee, wadda ’yar shekara 24 ce, ta zo Kaduna
inda ta ba Rediyon Nijeriya na Kaduna samfurin faifan ta don a rik'a
sakawa don mutane su ji inda ta koma. Wakilin mu ya samu mallakar
faifan, kuma ya saurarin wak'ok'i biyu da ke cikin sa.
Mujallar Fim ta tuntub'i Inyamiran da Zee-Zee ke huld'a da su,
kuma sun yi mana bayani kan wannan album da Zee-Zee ta ke shirin
fitarwa. Ta hanyar Inyamiran ne ma mu ka san cewa ashe sunan ta
na yanka Zainab. Wato Zainab Ibrahim; yanzu sunan da za ta rik'a
amfani da shi kenan, ba Ummi Ibrahim ba. Amma kuma sunan ta na harkar
wak'a shi ne Zee-Zee.
A bayani da masu kamfanin da Zee-Zee za ta yi wak'ok'in k'ark'ashin
su su ka ba mu, an nuna cewa mahaifin Zee-Zee Bafillace ne, yayin
da mahaifiyar ta take Balarabiya. Haka kuma sun nuna cewa Zee-Zee
ta na takardar shaidar karatu ta difloma a sashen kasuwanci (Business
Administration) daga Jami'ar Bayero, Kano.
Zee-Zee dai har ta kammala rikodin wak'ok'in ta, kuma sun yi wak'ok'in
ne tare da mawak'a irin su Weather man, Jonah D’ Monarch,
2solo na Dem Mama Records, Rha d’ Answer, da sauran su. A
yanzu haka ta na shutin d'in wata wak'a wai ita “Janglover”
a faifan bidiyo, inda Weatherman da Jonah D’ Monarch za su
fito a ciki.
An fi sanin Zee-Zee da bin wak'ok'i a finafinan Hausa, don haka
akwai alamun cewa wannan ba wani sabon abu ba ne. A cewar ta, za
ta koma yin wasan fim bayan ta gama da wannan album d'in na Turanci.
Za a k'addamar da album d'in a Legas da Kano, inji masu shirya mata
faifan.
Zee-Zee za ta kasance Bahaushiya ta farko da ta yi album d'in Turanci
irin na zamani. Idan kun tuna, Yakubu Muhammad da Sani Danja su
ne na farko da su ka yi album d'in Turanci a cikin ’yan fim
na Hausa, wato “Bolanle.”
Mun yi k'ok'arin jin ta bakin Zee-Zee kan wannan al’amari,
amma abin ya ci tura. Inyamiran da take tare da su sun hana ta yin
mu’amala ko magana da kowa. Wannan ya haifar da ji-ta-ji-a
a industiri da bayan ta. Wasu na cewa Zee-Zee ta zama budurwar mawak'i
Timaya ce, wai kullum ta na Legas a wurin sa. Wai za ma su yi aure.
Wasu kuma na cewa Inyamiran za su yi amfani da ita ne don su sami
kud'i, ganin cewa ita fitacciyar ’yar wasa ce a Arewa. Akwai
kuma masu cewa ko kad'an harkar wak'ok'in ’yan Kudu da Zee-Zee
ta koma bai dace da ita ba a matsayin ta na Bahaushiya kuma ’yar
Musulmi.
Zainab da Rabi’u
Dalle sun samu Umar
ABIN ba wuya! Auren fitaccen makad'i/mawak'in industiri Rabi’u
Dalle da mu ka ba ku labari a Fim a cikin 2008 ya yi albarka. Domin
kuwa kyakkyawar amaryar ta Rabi’u, wato Zainab, ta haifa masa
d'a namiji a ranar Asabar, 13 ga Yuni 2009, aka rad'a masa suna
Umar Magadad.
Zainab ta haihu ne a Asibitin Malam Aminu Kano da ke birnin Kano.
An yi bikin rad'in suna a unguwa Shagari Quarters a nan Kano. ’Yan’uwa
da abokan arzik'i da dama sun halarci bikin sunan. An kuma yi ruguntsumin
biki lafiya an tashi lafiya.
Allah ya raya Umar a cikin Musulunci. Mai jego kuma Allah ya k'ara
mata lafiya.
'ungiyar dillalai
na so a raba ta da zalunci
Daga IRO MAMMAN
K'UNGIYAR Dillalan Littattafai, Kayan D'ab’i da na Wasanni,
reshen Jihar Kano (Books, Stationary and Sports Dealers Association,
BSSDA), ta soki Hukumar Tace Finafinai da D'ab’i ta Jihar
Kano da yi mata barazana ta hanyar tilasta wa ’ya’yan
ta biyan kud'in rajista, wad'anda ta ce sun sab'a wa doka.
A wajajen watan Maris na bana, hukumar ta tab'a rubuta k'ungiyar
takarda inda ta buk'aci ’ya’yan ta da su je kowannen
su ya yi rajista a hukumar, inda zai biya kud'i N3,000, sannan ita
kuma k'ungiyar an ce ta biya N5,000 a kowace shekara.
To, sai k'ungiyar ta d'auki wani lauya, wanda ya jagorance su zuwa
Majalisar Dokoki ta Jihar Kano don karb'o kwafe na kundin dokar
da ta kafa hukumar. A nan ne su ka gano cewa ko kad'an hukumar ba
ta hurumin yin wata huld'a da k'ungiyar.
A bayanin da shugaban k'ungiyar, Cif Victor Okonkwo, ya yi wa manema
labarai kwanan baya kan halin k'ak'a- ni-ka-yi da k'ungiyar ke ciki,
ya ce sakamakon binciken da su ka yi, musamman kan Dokar Kafa Hukumar
Tace Finafinai ta Jihar Kano ta 2001, k'ungiyar ba ta k'ark'ashin
aikin hukumar.
Ya ce, “Mun karb'o kundin dokar daga Majalisar Dokoki ta
Jihar Kano kuma ta nuna b'aro-b'aro cewa babban aikin hukumar shi
ne kula da b'angaren finafinai da kuma gidajen silima, da kuma rubuce-rubucen
tsiraici. Ban ga abin da ya had'a su da k'ok'arin ganin mun yi rajista
da su ba. Mu mu na sana’ar sayar da littattafan manhaja ne
na d'aliban makarantun firamare da sakandare. Mun yi amanna da cewa
kamfanonin da ke wallafa su sun riga sun tace su.”
Ya ci gaba da cewa, “Bayan haka, mu na sha biyan haraji kala-kala
ga K'aramar Hukumar Fagge da kuma Ma’aikatar Ciniki ta jiha.
Zai kasance duka biyu idan kuma aka ce mu k'ara biyan wani sabon
harajin ga Hukumar Tace Finafinai.
“Mu ba mawallafa ba ne, kuma ba mu huld'a da littattafan
tsiraici. Mu na kira ga gwamnatin Jihar Kano da ta shigo cikin wannan
lamari don ta cece mu daga had'arin da mu ke ciki.”
Okonkwo ya k'alubalanci hukumar da ta kai k'arar k'ungiyar a kotu
domin tabbatar da manufofin dokar da ta kafa ta, ya na mai k'arawa
da cewa ko kad'an ba za su yarda a tatse ’yar ribar da su
ke ci ba ta hanyar haraji maras kan-gado da hukumomin gwamnati ke
son su biya.
Da aka tuntub'i shugaban hukumar don jin ta bakin sa, Malam Abubakar
Rabo Abdulkarim ya yi watsi da k'orafe-k'orafen k'ungiyar, ya na
mai cewa su hukuma su ne su ka fi kowa sanin tanade-tanaden dokar
hukumar, ba wani mutum da yake daga waje ba wanda ke ganin wai shi
ya san me dokar ta ce.
Ya ce da gaske ne dokar su ta shafi duk wani aiki na d'ab’i,
ciki kuwa har da masu sayar da jaridu da littattafai, na nishad'i
ne ko na makaranta. “Doka ta ba mu damar mu tabbatar da cewa
wad'annan dillalan littattafan su na sana’ar su bisa abin
da doka ta tanada, kuma tilas ne su zo su yi rajista mu ba su lasisi.
A kan haka ne mu ke aiki,” inji shi.
Shugaban hukumar ya yi barazanar cewa kwanan nan hukumar za ta
fara yak'i da wad'annan mutane, ya ce duk wanda hakan bai masa daidai
ba to ya tafi kotu ya yi k'ara.
An bugi ’yan
fim an hana su kuka
Daga ALIYU A. GORA II,
a Zariya
TUN ranar Litinin, 8 ga Yuni 2009, ’yan fim su ka samun sak'on
gayyata daga Cibiyar Nazarin Shari’ar Musulunci ta Jami’ar
Ahmadu Bello da ke Kwango, Zariya (Center For Islamic Legal Studies).
Cibiyar sun gayyaci ’yan fim ne da sunan cewa Darakta Janar
na Hukumar Tace Finafinai ta Jihar Kano, Malam Abubakar Rabo Abdulkarim,
zai zo ya yi lacca kan finafinan Hausa a ranar Lahadi, 21 ga Yuni.
A takardar gayyatar, an nuna cewa za a ba duk d'an fim d'in da ke
da abin cewa minti 10. Hakan ya sa ’yan fim, musamman manyan
cikin su a Kaduna, su ka yi shirin yadda za su b'ullo wa Rabo a
Zariya, mutumin da su ka dad'e su na neman yadda za su yi ido da
ido da shi.
Da yake an ce kyakkyawar Juma’a tun daga Laraba ake ganewa,
duk tattaunawar da ’yan fim d'in su ka yi a Zariya a k'ark'ashin
jagorancin shugaban k'ungiya furodusoshi ta Jihar Kaduna, ko muk'addashin
magatakardan k'ungiyar bai lek'a ba. ’Yan Zariyar kawai aka
bari su ka yi kid'an su, su ka kuma taka rawar su. Duk da haka,
kafin zuwan ranar da za a yi al’amarin, ’yan fim da
dama sun yi ta d'okin zuwan ranar don su je su yi gwa da gwa da
Rabo. Sai dai abin mamaki, har aka kammala babu wani d'an fim daga
Kaduna da ya lek'a ko K'ofar Doka.
Taron, wanda aka yi shi a d'akin taro na jami'ar, an fara shi da
misalin k'arfe 10:00 na safe kamar yadda aka tsara. Duk wani d'an
fim da ya kwana ya tashi a Zariya ya samu halarta. Rabo kuma ya
isa wurin da tawagar sa tun misalin k'arfe 9:30 na safe.
Bayan an gabatar da manyan bak'i, wad'anda ba sanannu ba ne, mafi
yawancin su malaman makarantar ne, sai aka ba Rabo fili kai tsaye
ya fara aiwatar da abin da ya kawo shi.
A jawabinn sa, Malam Rabo ya jadda cewa hukumar sa ba za ta bari
’yan fim su lalata kyawawan al’adu da addinin jama’ar
Kano ba. Ya ce gwamnatin Kano ba za ta tab'a yin sassauci kan aikin
ta na tsarkake jama’a ba da yin mulki bisa tanaje-tanajen
addini.
Rabo ya ce, “Mu ba mu na yak'i da kowa ba ne, to amma tilas
ne al’umma ta zauna ta san menene ya dace da ita kamar yadda
addinin Musulunci ya tanada. Ana cewa shi fim wani abu ne da ya
had'o da rayuwar d'an’adam, da al’adun sa, addinin sa
da kuma mu’amalar sa. Kamata ya yi ya yi mana jagora kan tunanin
mu da kuma yadda za mu gina nagartacciyar al’umma. Aikin da
ya rataya a wuyan mu ne, wanda ba za mu yi sassauci a kan aiwatar
da shi ba.”
Ya ce ’yan fim su ne su ka lalata harkar fim, kuma su ka
sa ana yi wa hukumar tace finafinai kallon hadarin kaji. Ya ce,
“Ku na so duniya ta kalle mu a matsayin al’ummar karuwai
da sauran ayyukan assha. Kuma ra’ayin mu shi ne fim ya na
da kyau a wani b'angaren, sannan ya na da rashin kyau a wani b'angaren.”
Haka dai Malam Rabo ya yi ta ragargazar ’yan fim, ya ci kasuwar
ya zauna.
Wani abin mamaki shi ne duk da cewa wad'anda su ka shirya laccar
malamai ne, amma da lokacin salla ya yi, rok'on mutane aka yi cewa
a hak'ura a ci gaba da sauraron jawabin Rabo domin, a cewar su,
wai lokacin salla ba ya wucewa, kuma abin da su ke yi d'in shi ma
aikin addini ne! Don haka ana ji ana gani azahar ta zo ta wuce,
har la’asar ta shigo, ba a tashi aka yi salla ba.
Wani abin da ya rikitar da ’yan fim shi ne da farko dai ba
a ce Rabo zai gabatar da k'asida ba, an ce dai zai zo ya yi “wa’azi
a kan alfanu da illolin finafinan Hausa,” kuma za a ba da
filin tambaya ga wanda ya ke da ita, wanda kuma ke da jawabi za
a ba shi minti 10. Amma sai da Rabo ya kwashe kimanin awa biyu cur
ya na jawabi bai dakata ba. Sannan daga k'arshe aka ce an ba ’yan
fim biyu dama su yi magana ta minti uku-uku kowannen su. Tsohon
shugaban K'ungiyar Furodusoshi ta Jihar Kaduna, Malam Adamu Bello
Ability, shi ne ya fara magana. Sai dai bayanin da ya gabatar ya
kashe wa ’yan fim jiki. Da farko, kasancewar an san Ability
d'an cara ne, ’yan fim sun yi tsammanin zai share masu hawaye
ta fuskar k'alubalantar Rabo gadan-gadan. Maimakon haka, sai ya
karkatar da akalar sa zuwa k'orafi a kan tsofaffin shugabannin Hukumar
Tace Finafinai ta Jihar Kano da cewa su su ka lalata harkar fim
kafin zuwan su Rabo. Wannan ya sa wasu ’yan fim d'in ke k'orafin
kamar Ability ya na yabawa ne da yadda Rabo ya ke ci wa harkar fim
tuwo a k'warya. Baya ga haka, Ability ya yi amfani da wannan dama
ya shaida wa Rabo cewa gyaran da ya ke kiran a yi wa sana’ar
fim, su a Zariya tuni sun yi nisa wajen shirye-shiryen d'auko masana
da za su koyar da yaran su yadda ake gudanar da harkokin fim. A
k'arshe, ya k'are jawabin sa da rok'on alfarma da cewa su na rok'on
Rabo ya ba su gudunmuwa kan hakan.
Shi kuwa shugaban K'ungiyar Furodusoshi ta Jihar Kaduna, Malam
Hamisu Jibril Goma, k'alubalantar Rabo ya yi kai-tsaye a kan wani
misali da ya bayar na cewa a Turai an yi wani fim da ya ke ganin
kamar an ci zarafin Musulunci ne. Ya ce ya na ganin haka ya kamata
a ce ’yan fim d'in Hausa su rik'a yi wajen d'aukaka addini
da al’adun su. Shugaban ya k'alubalanci Rabo da cewa me ya
sa hukumar sa ba ta shirya wani fim makamancin wancan d'in ba don
mayar da martani? A k'arshen jawabin sa kuma ya jaddada wa Rabo
cewa su a Jihar Kaduna su na da tsari na shugabanci da doka. Shi
ya sa shi kan sa Rabo a jawabin sa ya keb'e
Kaduna da cewa ba ta daga cikin garuruwan da ake zargin ’yan
fim sun gurb'ata, ko da ya ke dai ya ce garin Zariya ya na buk'atar
garambawul.
Fahimtar da mafi yawacin jama’ar da su ka halarci taron su
ka yi wa al’amarin ita ce da ma wad'anda su ka shirya laccar
mutane ne da su ke k'yamar sana’ar fim da masu yin ta tun
asali, ba ma su son a gyara kurakuran da ke ciki ba. Hakan ya tabbata
ne a lokacin da wani malami mai suna Ahmed Bello Dogarawa, wanda
ya ke d'aya daga cikin jiga-jigan malaman da su ka shirya taron,
a jawabin sa na k'arshen taron ya ce ba ya son fim, ba ya son d'an
fim, ba ya son ganin d'an fim, kuma babu abin da d'an fim zai yi
ya birge shi a rayuwa.
“A gaskiya ba a yi wa ’yan fim adalci ba. In ba haka
ba, ya za a tasa su a gaba ana ragargaza, amma aka hana su isasshen
lokacin da su ma za su gabatar da nasu k'asidun?” inji wani
d'alibi da ke zaune kusa da wakilin mu a wurin.
Akwai wani d'an fim da ya rik'a yunk'urin a ba shi dama ya yi magana.
Amma nan take wani da ke kusa da shi ya ba shi shawara da cewa ya
yi hak'uri. In kuwa ya kuskura ya fad'i abin da ya sab'a wa ra’ayin
Rabo a wurin, zai sha kashin tsiya. Saboda akwai tunanin tarko ne
aka d'ana wa ’yan fim d'in ko za a samu wanda zai yi maganar
da ta sab'a wa mak'asudin taron. Da yawa sun yarda da wannan hasashen,
musamman ganin yadda shugaban taron, Malam Ahmed Bello Dogarawa,
ya tsare gida, wanda tun da aka fara har aka kammala babu wanda
ya ga ko murmushin sa, don kada ma ’yan fim su yi tunanin
samun sakin fuskar da zai iya sauraren su.
Bayan an fito daga d'akin taron, wakilin mu ya ji wani furodusa
na cewa, “Wai ni me ya sa ma mu ka zo wannan wurin? Da na
san an gayyato mu ne don a ci zarafin mu, wallahi da ban zo ba.
Amma, gobe ma rana ce!”
An kammala taron lafiya da misalin k'arfe 3:00 na yamma. Manyan
’yan fim da su ka halarci taron sun had'a da Aminu Mirror,
Musa Aminu (Carlos), Tukur Aliyu, da kuma Cashman. ’Yan wasa
kuma da dama sun samu halarta, amma duk na cikin garin Zariya. |