BABBAN LABARIN

BA SOYAYYA TA KAWO NI INDUSTIRI BA
SAFIYA AHMED

 

KYAKKYAWA CE - SON KOWA KIN WANDA YA RASA. SANNAN GWANA CE WAJEN IYA WASAN FIM. GA TA DA FARIN JINI A WURIN ’YAN FIM DA MASU KALLO. SHIN MENENE RA’AYIN SAFIYA AHMED KAN HALIN DA INDUSTIRI KE CIKI?

Daga SANI MAIKATANGA

GASKIYA ne da masu iya magana su ka ce mutuwar wani tashin wani. A daidai lokacin da hasken wasu taurarin ya ke dushewa, ita Safiya Ahmed lokacin ne nata yake k'ara haskawa. Ba ta dad'e da shigowa industiri ba, amma saboda cin sa'ar shigowa harkar da k'afar dama, kusan yanzu za a iya lissafa ta cikin fitattun taurari masu tasowa.

Da ya ke mafi yawanci finafinan da ta yi ba su riga sun shiga kasuwa ba, 'yan kallo da dama za su yi mata kallon bak'uwa. Sai dai a cikin industiri, duk wanda ya kai ya kawo ya san da zaman ta.

Kai da ganin ta ka san ta dace a ce ita ce jarumar fim d'in ka. Ga ta dai da kyau, ga kyan launin fata, ga kyan diri, ga fara’a, ga tsafta, ga natsuwa da biyayya musamman ga na gaba da ita. Sannan jarumar ta samu shaidar zama d'aya daga cikin jaruman da ba su cika tsegumi ba a lokacin da ake aikin fim a lokeshin.

Sai dai abin tambaya game da Safiya shi ne, me ya sa ita yanzu ta ga wurin zama a industiri, yayin da wasu ke rantawa a na kare su na canza alk'ibla? Me ta ke ciki? Menene burin ta dangane da harkar fim? Ya zancen auren ta? Menene matsayin ta ga gwamnatin Jihar Kano? Shin ita ma ta na da ubangida kamar yadda sauran taurari mata su ke yi? Jarumar duk ta amsa wad'annan tambayoyin da ma wasu a tattaunawar musamman da ta yi da wakilin mu kwanan baya a birnin Kano.

FIM: Safiya, kwana biyu. Yaya industiri?

SAFIYA: To, ga mu nan a ciki ana gogawa.

Me za ki iya cewa game da halin da industiri ta shiga?

Babu abin da za mu ce sai dai mu ce Allah Ya sa haka shi ne mafi alkhairi. Allah Ya gyara mana wannan sana’a tamu. Kuma duk abin da ka ke yi a rayuwa da ma in har ba a jarrabe ka ba a kan abin da ka ke yi, to ya kamata kai ma ka tambayi kan ka.

Har yanzu kenan ki na cikin harkar ba ki bar ta ba, kamar yadda wasu su ka yi. Ke me ya sa har yanzu ana gogawa da ke?

Alhamdu lillahi. Gaskiya ni dai babu abin da zan ce, domin kusan d'aukaka ce ta zo bayan komai ya d'an lafa. Finafinan da aka rik'a yi a wajen Kano kusan duk da mu aka rik'a yi. Ak'alla yanzu ina da finafinai manya da ni ce na ke jan su. Misali kamar fim d'in ‘Fargaba’, ‘Mai Doki’, ‘Biyayya’, da dai sauran su.

Yanzu a k'ark'ashin wane kamfani ki ke?

Ina nan a kamfanin ubangida na Jamilu mai kamfanin Almubarak.

Amma da muka ji an ce kin koma kamfanin 2-Effects...

A’a, ina nan a kamfanin ubangida na. Su ma 2-Effects kamar kamfani na ne, domin suna taimaka min. Su na yi min finafinai, don ko 'Mai Doki' ma fim d'in kamfanin su ne.

Menene yanzu ki ke ganin ya sa ana ta gayyatar ki yin finafinai?

Ka san komai daga Allah ne. Ina ganin lokaci ne, domin komai ka gani daga Allah ne. D'aukaka ce na samu daga Allah.

Duk finafinan da ki ka yi yanzu a ina aka yi su?

An yi wasu a Kaduna, wasu kuma a Abuja.

A cikin finafinan da ki ka yi yanzu wanne ne ki ka fi so, ko ki ka fi shan wahala, ko kuma wanda ba ki tab'a yin irin sa ba?

Fim d'in ‘Fargaba’ shi ne fim d'in da ban tab'a yin irin sa ba. Kuma fim d'in ya burge ni sosai. Sannan kuma fim d'in ‘Biyayya’, shi ne fim d'in da na sha wahala a cikin sa. Sannan irin yadda a fim d'in 'Fargaba', ko yaushe ina cikin fargaba, ya sa kusan ji na ke kamar ma da gaske ake yin komai. Kuma irin rol d'in da Baballe da A'isha Abaab su ka hau ya burge ni. Sannan kuma fim d'in ya ci sunan sa, domin kusan kowa a fim d'in a cikin fargaba ya ke, kai ka ce da gaske ake yin komai a fim d'in.

Kin ambaci wani fim mai suna 'Biyayya', shi kuma na wanene?

Fim d'in Hafsat Sulaiman ne. Wannan fim d'in na sha wahala a cikin sa ba kad'an ba.

A kan me fim d'in ya ke nuni har ki ka ce kin sha wahala sosai a cikin sa?

Fim d'in ya na koyarwa ne kan irin yadda iyayen miji su ke takura wa matar d'an su, da d'ora mata abin da ba ita ta yi ba.

An ce ki na da alak'a da ita Hafsat. Mecece dangantakar ku da ita?

Baba ce a wuri na. Yayar ta ta na auren wan baba ta.

Ga shi yanzu kin halarci bikin Binta da Tahir, ke kuma yaushe za a yi naki?

Lokaci na ke jira. Domin da mutuwa da aure duk lokaci ne na Ubangiji. Ina nan ina rok'on Allah Ya kawo min mai so na. Su kuma da Allah Ya k'addara nasu auren yanzu, ina yi masu fatan alkhairi da zaman lafiya da kuma zuri’a d'ayyiba.

Ki na nufin ki ce har yanzu ba ki da saurayi, ko da a industiri?

Ba ni da saurayi a industiri. Amma ina da ubangida. Ni sana'ar fim ta kawo ni ba wannan ba.

Ki na ganin za ki iya yin aure a daidai wannan lokacin da za a iya cewa ke ma tauraruwar ki ta na haskawa?

Me zai hana ni yin aure? Ai in ka ga ban yi ba ko ba a yi ba, to lokacin ne bai yi ba. Amma muddin lokacin ya yi, za ka ga sai dai labarin Safiya a industiri.

Kusan duk jaruman industiri sun yi rajista da gwamnatin Jihar Kano. Ke ma kin yi ko yaya?
Na’am, na yi rajista ni ma.

Menene dalilin ki na yin rajista da gwamnati?

Kawai na fuskanci cewa gwamnati ta na son yin gyara ne a wannan harkar tamu. Kuma duk wani abu da ya faru a baya game da wannnan harkar, kawai mu ajiye shi a gefe, mu tsaya mu had'a kan mu. In dai mu ka yi wannan, to duk wani mai neman nak'asun mu zai yi ma ya bari.

Ki na ganin shigowar gwamnati a harkar fim da alamun wasu abubuwan na ci gaba ne?

Gaskiya duk wani abu, kamar yadda na ce, in ka na yi har ba ka samu matsala a ciki ba to ka tambayi kan ka. Akwai alamun ci-gaba shigowar gwamnati cikin harkar nan.

Menene kiran ki ko shawara ga abokan sana’ar ki?

Kira na ba ya wuce in ce mu ci gaba da yin addu’a. Kuma ina kira da mu ji tsoron Allah, mu so junan mu.

RAYUWAR IYALI
BABBAN LABARIN
 
 

WASIKU
Ku daina wulakanci
Ai ga irin ta nan!
Mu taya sani addu’a
Abin a yaba ne
Allah ya gafarta ma ta
Allah ya jikan jamila
Allah ya jikan binta
Sakon ta’aziyya da jaje
Ta’aziyya ga sheme
Ki canza rayuwar ki
Allah ya gafarta ma ta
Sako ga shehu kano
Mu ma mun sara mata
’Yan fim ga shawara
Dubi dai jamila haruna
jaje da ta’aziyya
Allah jikan rai
Aikin ku ya yi kyau
Matashiya ga ummancy
‘bolanle’ shirme ne
Ku hada ni da ali nuhu
Rashin ya shafi kowa
Allah ya ba sani lafiya
Sakon ta’aziyya
Fati nijar ta birge ni
Gaisuwa ga ma’aurata
Ku daina la’antar su
Ki na fa da aure!
Rabo mayaudari ne
Allah jikan su
Tahir da binta ina murna
A gaida nakwango
Fantimoti ga gyara
Na ga alfanun fim

LABARAI
An yi taron addu’a ga mamatan marubuta a Kano
’Yan fim na Katsina sun kai wa Rabo caffa
Kotu ta haramta wak'ok'in industiri guda 11
Jami’an Rabo sun fara farautar mawak'a
An Kama Ali Jita Saboda Wak'ar Biki
Mahaifiyar Safiya Musa Ta Kwanta Dama
Ummi Zee-Zee ta zama mawak'iyar Turanci
Zainab da Rabi’u Dalle sun samu Umar
K'ungiyar dillalai na so a raba ta da zalunci
An bugi ’yan fim an hana su kuka
 
   
 
An fara buga mujallar Fim (ISSN 1595-7780) a cikin Maris 1999. Ta na fitowa a kowane wata daga kamfanin INFORMART PUBLISHERS LTD., No. AK 6, Yoruba Road, Kaduna, Nijeriya. Ofishin mu a Kano: Ofishin mujallar Concern, 2nd Floor, Hadiza House, daura da Masallacin Umar Ibn Khattab, Zaria Road, Kano.
A aiko da dukkan wasiku ta adireshin mu na I-mel: mujallarfim@yahoo.com