|
RABO DA MARUBUTA SUN MAIDA WUK'AR
Sakamakon zuwan da shugabannin k'ungiyar ANA
ta k'asa su ka kawo birnin Kano, akwai alamun
samun sa’ida tsakanin marubutan Kano da
Hukumar Tace Finafinai da D'ab’i ta Jihar
Kano a kan rikicin tace littattafai da marubuta
Daga SANI MAIKATANGA da IBRAHIM MUSA GIGINYU,
a Kano
DA alama, takun saar da ya fara faruwa tsakanin
marubutan littattafai da Hukumar Tace Finafinai
da D'ab’i ta Jihar Kano zai ragu idan har
aka aiwatar da yarjejeniyar da aka cimmawa a ranar
25 ga Agusta, 2008. A ranar, shugaban {ungiyar
Marubuta ta Nijeriya (Association of Nigerian
Authors, ANA), Dakta Wale Okediran, ya kai ziyara
a Hukumar Tace Finafinai da D'ab’i ta Jihar
Kano don ganawa da shugaban hukumar, Malam Abubakar
Rabo Abdulkarim. Ziyarar ta biyo bayan sa-katsi-sa-tokan
da ake yi ne tsakanin marubutan, wad'anda hukumar
ta ce za ta fara yi wa rajista, su kuma su ka
ce ba su yarda ba. An yi cacar baki tsakanin jami'an
hukumar da marubutan a wurare da dama. Ziyarar
su Okediran ta faru ne don neman sasanta b'angarorin
biyu.
Tun kafin a shiga d'akin ganawar, sai da aka
aiwatar da wani taro tsakanin hukumar tace fiafinai
da kuma jami'an k'ungiyar ta ANA.
Da fako dai shugaban na ANA ya fara ne da mik'a
godiyar sa ga Malam Rabo bisa amincewar da ya
yi kan gudanar da wannan ganawar. Ya kuma buk'ace
shi da ya mik'a masa sakon fatan alheri ga Gwamnan
jihar saboda irin goyon bayan da ya ke ba wa marubuta
a jihar. Ya ci gaba da cewa ba zai tab'a mancewa
da Kano ba, domin a taron marubuta na k'asa baki
d'aya da aka yi a Kano a cikin 2005, shi ne ya
samar da wannan shugabanci nasa da na sauran shugabannin
kwamitin zartaswa na ANA.
Ya ce, “Kano jiha ce mai cike da d'imbin
tarihi na rubuce-rubuce. Saboda haka 'ya'yan ANA
da ke wannan jihar ke da matuk'ar k'ima a idon
marubuta na gida da ma na waje. Dalilin kenan
da ya sa mu ke ganin duk wani abu da ya samu ANA
ta Kano to wannan abin ya shafi ilahirin duk wani
marubuci da ke wannan k'asar.”
Okediran ya ci gaba da yin bayani kamar haka:
“Na tsaya gaban wannan taron bisa doron
tsari irin na ci-gaban d'an’adam don gabatar
da ra'ayin k'ungiyar mu a kan batun rubutu da
kuma maganar tacewa wanda wannan ya kasance matsalar
da ta k'i ci ta k'i cinyewa a wannan jiha mai
girma, wato Jihar Kano.
“Tun lokacin da kafafen yad'a labarai su
ka fara d'aukar wannan labari, mu a matakin shugabanci
a wannan k'ungiya mun fahimci cewar akwai matsala
ta fahimta. Domin mu mu na gani matsalar ba matsala
ba ce wacce za a kasa shawo kan ta ta hanyar zama
bisa teburin shawara da kuma tattaunawa don fahimtar
juna. Hakan shi ya sa mu ka yi maza-maza mu ka
amsa kukan ’ya’yan wannan k'ungiya
da ke Kano. Ba za mu nad'e hannuwan mu ba ga duk
wani abu da zai kawo mishkila ga damar da marubuci
ke da ita wajen yin rubutu da bugawa. Kuma wannan
ba ya na nufin mu na adawa da tattaunawa da Hukamar
Tace Finafinai da D'ab’i ba ne don samun
maslaha; hasali ma ina mai farin ciki da wannan
damar ta samu a yau d'in nan, 25 ga watan Agusta,
2008.”
Da ga nan shugaban ya yi bayani mai tsayi kan
yadda aka samar da k'ungiyar ANA shekaru 26 da
su ka wuce, k'ungiyar da a yanzu ta ke da rassa
a jihohi 36 da ke wannan k'asar. Shugaban ya yi
bayani kan yadda k'ungiyar ke ba da gudunmuwa
wajen gina k'asa ta b'angaren ilmi, ci-gaban al’adu,
zaman lafiya, da dai sauran su.
Okediran ya yi tsokaci game da yadda marubuta
su ke kasancewa, inda ya ce, “Muhalli, ilmi,
k'warewa da sauran su na da matuk'ar tasiri a
kan marubuci. Wannan na nufin ’ya’yan
ANA na Kano na sane da nauyin da ke kan su na
kare addinin su, al’adar su, wajen samar
da ingantattun littattafai. Duk da cewar mazauna
Kano ne amma sun san rubuce-rubucen su ba na iya
Kano kad'ai ba ne, har da duniya baki d'ayan ta.
Haka zalika k'ungiyar ANA ba za ta amince da duk
wani nau’in rubutu wanda zai iya gurb'ata
tarbiyya ko al’ada ba. Ga mu ’yan
k'ungiyar ANA, buk'atar marubuci ya kawo littafin
sa a tantance kafin a ba shi dama ya buga, nak'asu
ne ga fasahar sa, domin tarihi ya nuna ba a tab'a
yin haka ba. Kuma yin hakan ba zai haifar wa Jihar
Kano wata martaba ba gida da waje.”
A k'arshe, shugaban ya mik'a goron gayyata ga
hukumar zuwa wajen taron marubuta na duniya, wato
Annual International Convention karo na 27 da
za a gudanar a ranar 31 ga Oktoba, 2008 a Gusau,
Jihar Zamfara.
A nasa jawabin, Malam Rabo ya nuna farin cikin
sa da samun damar karb'ar bak'uncin shugaban na
ANA. Ya kuma nuna jin dad'in sa bisa wannan zama
da za a yi na tattaunawa, wanda shugaban ya ce
sun dad'e suna neman a yi hakan amma abin ya ci
tura. Haka zalika ya nuna rashin jin dad'in sa
ga yadda kafafen yad'a labarai su ka yi ta fuskantar
al’amarin ta bari d'aya kawai, inda ya ce,
“Abin b'acin rai ne yadda na ga mutane akilai
na yin rubuce-rubuce marasa manufa wad'anda su
ka karkata b'angare d'aya kawai. Duk da wannan
bai sa mun d'au al’amuran da zafi ba, sai
mu ka yi amfani da hankali, kasancewar amfani
da hankali na d'aya daga cikin abin da aka raine
mu bi san sa.”
Shugaban ya ci gaba da cewa ya ji dad'in yadda
a bayanin sa, Okediran ya fahimci cewar akwai
matsala ta fahimta. Ya k'ara da cewa bayan wannan
akwai matsala ta yad'a ji-ta-ji-ta da gangan don
alak'anta wannan maganar ta marubuta da wata magana
da ba ta marubuta ba. Domin, inji shi, akwai ’ya’yan
ANA masu gida biyu, wato marubuta ne kuma watak'ila
masu harkar fim ne, ko masu gudanar da gidajen
sinima, da dai makamankan hakan. Kasancewar harkar
fim, sinima da sauran ire-iren wannan harkar duk
su na k'ark'ashin kulawar wannan hukumar ne.
Rabo ya yi murna da kuma karb'ar goron gayyatar
da k'ungiyar ANA ta mik'a masa na taron da za
ta yi a Gusau. A k'arshe ya ce, “Doka ita
ta kafa mu, kuma ba za mu kasance masu wofinta
doka ba. Saboda haka duk wani abu da za mu yi,
za mu yi shi ne bisa farfajiyar da doka ta tanadar.”
Daga nan sai aka kori ’yan jarida. Sannan
b'agarorin biyu su ka shiga tattaunawa ta sirri,
wanda wannan tattaunawar ta kai ga samar da takardar
bayan taro wacce kuma aka rarraba wa ’yan
jaridu ita.
A tsarin wannan ziyarar shugaban na ANA ta k'asa
zai gana da Mataimakin Gwamnan Jihar Kano a Gidan
Gwamnati na Kano a ranar Talata, 26 ga Agusta,
2008.
Haka kuwa aka yi. Washegari, shugaban na ANA
ya kai ziyara Gidan Gwannatin inda mai girma Mataimakin
Gwamna, Injiniya Abdullahi Muhammed Gwarzo, ya
karb'e shi tare da ’yan rakiyar sa, wad'anda
su ka had'a da shugabannin rassan k'ungiyar daga
jihohin Kano, Katsina, Zamfara da Sakkwato. A
bayanin sa, Dakta Okediran ya sanar da mataimakin
gwamnan cewa shugabancin ANA na k'asa da kuma
Hukumar Tace Finafinai da D'ab’i ta Jihar
Kano sun zauna a jiya don samun fahimta da kuma
damar gudanar da ayyukan su kan tafarkin taimakekeniya.
Ya k'ara da cewa cikin matsayar da aka cimma
har da amincewar da hukumar ta yi na a gudanar
da taron k'ara wa juna sani wanda za ta gudanar
nan ba d'a dad'ewa ba. Ya kuma nuna farin cikin
sa bisa karb'ar goron gayyatar zuwa babban taron
ANA na k'asa da za a gudanar a Gusau da hukumar
ta yi. Ya ce, ‘‘Ina mai amfani da
wannan damar wajen yaba wa mai girma Gwamnan Jihar
Kano saboda irin gudunmawar da ya ke ba harkar
ilmi a Jihar Kano. Haka kuma mun lura da cewa
d'akin karatun da ke ofishin mataimakin gwamna
na fama da matsakar rashin littattafai. Sabod
haka mu ke masu amfani da wannan dama wajen ba
da gudunmuwar littattafai ga wannan d'akin karatu.
A matsayin wani b'angare na fatan alkhairi ga
gwamnati. Mu na masu godiya da wannan dama da
aka ba mu, kuma mu na masu addu’ar Allah
Ya ci gaba da yi wa wannan gwamnati jagora.”
A nasa jawabin, Injiniya Abdullahi Muhammad Gwarzo
ya mik'a sak'on maraba ga shugaban na ANA na k'asa
a madadin gwamnan jihar da mutanen jihar. Ya kuma
k'ara ba da hak'uri bisa jinkirin da aka samu
wajen ganawar tasu. Ya ci gaba da cewa, “Gwamnati
wannan jiha gwamnati ce mai bai wa kowa ’yancin
sa yadda tsarin mulkin k'asa ya shimfid'a. Haka
zalika aikin mu ne mu d'ora jama’a bisa
wannan turbar, dalihin da ya sa aka kafa wannan
hukumar ta tace finafinai da d'ab’i.”
Mataimakin gwamnan ya yi wata magana wadda ta
dad'ad'a wa k'ungiya ANA rai sosai har sai da
ta kai da an tafa masa. Maganar kuwa ita ce: ‘‘Hak'k'in
wannan hukumar ne sa ido a harkar rubuce-rubuce,
talifi da kasuwancin littattafan. Na yi matuk'ar
namaki da wai marubuta kan su an sako su cikin
wannan tsarin. Na san kun sami zama a jiya, kun
kuma cimma matsaya. Mu kuma a nan a shirye mu
ke da mu yi aiki da duk wata yarjejeniya da wannan
zama naku ya samar. Kuma ina mai fatan wannan
matsaya da aka cimma zai amfana mana mu da mutanen
Kano baki d'aya.’’
Injiniya Gwarzo ya kuma yi wa ’ya’yan
ANA ta Kano albishirin cewa gwamnatin jihar za
ta d'au nauyin su wajen halartar taron k'ara wa
juna sanin da za a yi. Ya kuma yi kira ga ’ya’yan
k'ungiyar ta ANA da su isar da wannan sak'on na
gwamnati ga duk wani memba nata. Ya kuma yi kira
da cewar babu wata hujja ta sa-in-sa tsakanin
gwamnati da k'ungiyar marubutan, domin dukkan
su abokan aiki da juna ne. A k'arshe ya yi wa
shugaban ANA ta k'asa fatan alkhairi da kuma addu’ar
Allah Ya mai da shi gida lafiya.
Haka dai aka fito daga taron ana ta murmushi
da jinjina wa juna. Kowa ya na da yak'inin cewa
wannan zama da aka yi da Malam Rabo da kuma mataimakin
gwamna ya kawo k'arshen sa-in-sar da ta shiga
tsakanin marubutan da gwamnati. To amma wani jami’i
na k'ungiyar ANA ta Kano ya yi gargad'in cewa
kada marubuta su yi sakacin yin barci da dukkan
idanun su a rufe. Ya ce ya kamata a ci gaba da
sa ido kan abubuwan da hukumar Rabo ta alk'awarta,
“domin ba mamaki Rabo ya k'ara zuwa gidan
rediyo ya b'ata marubuta - saboda haka ya dinga
yi wa 'yan fim bayan sun yi zaman sasantawa.” |